An kai harin ta'addancin ne a garin Hilla wanda ke kilomita dari daga kudancin birnin Bagdaza, kuma tuni kungiyar Daesh ta dauki alhain kai harin a wani sakon da ta aike a cikin yanar gizo.
Majiyar asbitoci da na yansanda sun bayyana cewa mutocin masu ziyarar arba'in guda biyar ne harin kunan bakin waken ya shafa. Labarin ya kara da cewa mutanen sun tsaya a wurin ne don cin abinci a cikin wani dakin cin abinci kusa da wurin kafin bom din ya tashi.
Wannan dai shi ne hari na farko mafi muni wanda kungiyar daesh ta kaiwa musulman shia wadanda take daukarsu kafirai, wadanda kuma suka yi ruwa da tsaki wajen yakar Kungiyar a tungarsu ta karshe a birnin Musil na kasar Iraqi daga ranar sha bakwai ga watan da ya gabata.