IQNA

Ban ki Moon Ya Bukaci Kawo Karshen Killace Gaza

16:28 - December 17, 2016
Lambar Labari: 3481044
Bangaren kasa da kasa, Babban sakataren majalisar dinkin duniya mai barin gado Ban ki Moon ya bukaci da akawo karshen killace yankin zirin Gaza da haramtacciyar kasar Isra'ila ke yi.
Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa, Ban Ki Moon ya yi wannan kira ne a jiya, a daidai lokacin da 'yan kwanaki ne suka rage ya bar ofishin nasa wanda ya kwashe tsawon shekaro goma a cikinsa.

Moon ya ce ya zama wajibi Isra'ila ta janye daga yankunan Palastinawa da take rike da da su tun daga shekara ta 1967, domin kuwa a cewarsa hakan ya sabawa dukaknin dokokinna kasa da kasa.

Kamar yadda kuma ya bayyana cewa fiye da mutane dubu 600 ne suke cikin mawuyacin hali a yankin an Gaza sakamaon killacewar da Isra'ila take yi wa yankin tsawon shekaru, wanda shi ya saba wa dukkanin kudurori na majalisar dinkin duniya.

Wannan furuci na Ban Ki Moon dai bai zowa kowa da mamaki ba, kasantuwar cewa ya kwashe tsawon shekaru goma a jere yana rike da mukamin babban sakataren majalisar dinkin duniya, amma bai taba furta cewa mamayar yankunan Palastinawa da Ira'ila ke yi ya sabawa kaida da doka ba sai yanzu, da ya rage sauran yan kwanaki da ba su mako biyu ba ya bar ofishin.

3554443


Abubuwan Da Ya Shafa: iqna ya zama wajibi
captcha