IQNA

Mahukuntan Mayanmar Za Su Kori Musulmi Daga Yankunansu

21:17 - December 27, 2016
Lambar Labari: 3481075
Mahukuntan Mayanmar Za Su Kori Musulmi Daga Yankunansu
Bangaren kasa da kasa, Gwamnatin kasar Myanmar na shirin raba wasu musulmi da yankunansu, tare da zaunar da wasu 'yan addinin Buda a cikin yankunan nasu a garin Mangdo da cikin lardin Rakhin.
Kamfanin dilalncin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga kamfanin dillancin labaran Arakan ya bayar da rahoton cewa, mahukunta a lardin Rakhin na kasar Myanmar, sun gina wasu kauyuka guda bakwai a wasu yankuna da ke cikin lardin na Rakhin, da nufin zaunar da musulmi da suke a garin Mangdo.

Mahukuntan suka ce asalin garin Mangdo na mabiya addinin Buda ne, amma daga bisani 'yan kabilar Rohingya da suka shigo cikin kasar daga Bangadasha suka zauna wurin, a kan haka mabiya addinin Buda za su dawo wurinsu, yayin da muuslmin da ke wurin za a mayar da su zuwa kauyukan da aka gina musua wasu wuraren na daban.

Fiye da kashi 98 na mutanen da suke zaune a wannan gari dai mabiya addinin muslunci ne 'yan kabilar Rohingya, yayin da adadin masu bin addinin Buda a garin bai wuce kashi 2 cikin dari ba, kuma muuslmi suna zaune da su lafiya tsawon daruruwan shekaru ba a taba jin tsakaninsu.

Kimanin watanni da suka gabata ne dai jami'an tsaron gwamnatin Myanmar suka yi wa musulmi kisan gilla a wannan yanki, tare da kone musu gidaje da kaddarori.

3557068


captcha