IQNA

Abbas Shoman:

Isar Da Sakon Muslunci Ga Isra'ila Ba Shi Da Alaka Da Azhar

22:33 - December 29, 2016
Lambar Labari: 3481079
Bangaren kasa da kasa, mataimkin babban malamin Azhar ya mayar da martini kan kiran da wani mai bincike ya yin a a kai sakon kira zuwa ga muslunci ga yahudawan Isra'ila.
Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na Alfajr cewa, Abbas Shoman ya bayyana cewa, kiran da Umar salim mai bincike dan kasar Amurka kuma dan asalin kasar Masar ya yi kan cewa Azhar ta bude ofishinta na isar da sakon muslunci a cikin Isra'ila, wannan kira bas hi da wata alaka da Azhar.

Yace hakika wadanda suke da irin wannan tunani ga alama sanyi ya taba kwakwalensu ne har suka manta da Isra'ila da kuma matsayinta dangane da muslunci.

Tun kafin wannan lokacin da Umar salim ta bata yin wani kira makamancin wannan na neman a kulla alaka takanin Azhar da Isra'ila, wanda hakan ya sanya malamajn Azhar fitar da fatawar barranta da shi.

Mutumin dai ya kwashe tsawon shekaru a kasar Amurka, wanda ake zarginsa da cewa yana daga cikin masu yi ma yahudawa aiki a kasashen muslmi, sakamakon yadda yak efitowa afili yana kare manufofin Isra'ila a duniya.

3556805


captcha