IQNA

Dakarun Iraki Sun Kwace Majami'ar Sa'a da Da Masallacin Umar Aswad A Mausul

21:06 - June 29, 2017
Lambar Labari: 3481655
Bangaren kasa da kasa, dakarun kasar Iraki sun kammala kwace muhimman wurare a cikin tsohon garin Mausul da ya rage a hannun 'yan ta'addan takriyyah na ISIS.
Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa, dan rahoton tashar alalam daga birnin mausul ya bayar da rahoton cewa, a yau dakarun Iraki sun shiga cikin majami'ar Sa'a da kuma masallacin Umar Aswad, wadanda su ne muhimman wuraren da suka rage a hannun 'yan ta'addan ISIS a garin Mausul.

Abdulamir Rashid Yarallah babban jami'in rundunar kwato lardin Nainawa daga hannun 'yan ta'addan takfiriyya ya bayyana cewa, sun gama karya lagon kungiyar a Mausul, domin kuwa majamia'ar Sa'a da kuma masallacin Umar Aswad a halin yanzu na hannun dakarun Iraki.

Ya kara da cewa yanzu haka sauran 'yan ta'adda da suka rage sun tarwatse, kuma an aci gaba da bin sawunsu domin tabbatar da cewa babu ko daya daga cikin 'yan ta'addan da ya yi saura a cikin Mausul da ma lardin na Nainawa baki daya.

Tuna cikin shekara ta 2014 ce Ibrahim Samirra'i wanda ake yi wa lakabi da Abubakar Albaghdadi, tare da taimakon wasu daga cikin kasahen larabawa, ya jagoranci dubban mayakan 'yan ta'addan takfiriyya daga kasashen duniya daban-daban, wajen mamaye wasu yankuna na kasar Iraki, da sunan kafa daular Islama.

3613888


captcha