Rahoton ya ce jami'an tsaron sun harbe wani magidanci mai sun Muhsen Al'aujami a lokacin da ya fito bakin kofar gidansa a yammacin jiya.
Haka nan kuam wasu rahotonnin sun baya ga wannan magidancin sun kara harbe wani matashi, kamar yadda akuma suka harbe mutane 3 da suke rayuwa a cikin garinsu a tsakanin danginsu ba tare da wani dalili ba.
Kungiyoyin kare-hakkin bil adama na duniya sun yi tir da Allah wadai da abin da suka kira bakin mulki na kama karya a kan fararen hula 'yan masu cikakken hakki, tare da yin kira ga majalisar dinkin duniya ta gaggauta daukar matakin takawa mahukuntan masarautar 'yan'yan gidan Saud birki kan kisan gillar da suke wa fararen hula saboda dalilai na siyasa.