A cikin bayanin kungiyar ta bayyana cewa, mutanen irin su Aung San Suu Kyi ba su cancanci samun lambar yabo ta zaman lafiya ta nobel ba, idan aka dubi irin kisan kiyashin da gwamnatinta take yi wa musulmi a kasar Myanmar.
Bayanin ya ci gaba da cewa, kisan kiyashin da ake yi wa musulmi a halin yanzu haka akasar Myanmar, lamari ne da ya cancanci dukkanin kasashen duniya su dauki matakin ladabtarwa a kan gwanatin kasar Myanmar a kansa, sakamakon kisan dubban muusulmi 'yan kabilar Rohingya a cikin kasa da mako guda.
Haka nan kuma bayanin ya bukaci da a gurfanar da Aung San Suu Kyi a gaban kotun manyan laifuka ta duniya domin ta fuskanci hukunci.