Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta
cewa, ya nakalto daga shafin yada labarai na africanindy cewa, wannan lamari ya
faru ne a ranar Talata da ta gabata, wanda kuma hakan ya bayar da mamaki
matuka.
Wannan masalalci dai kwamitin musulmi jamus 'yan asalin Turkiya ne suka gina shi, kuma wannan kwamiti nasu ya gina masallatai fiye da 900 a fadin kasar ta Jamus.
Hukumar da ke sanya ido kan harkokin zamantakewar jama'a a kasar Jamus SETA ta sanar da cewa, kyamar musulmi na karuwa matuka akasar a cikin lokutan baya-bayan nan, inda hare-haren suka ninka daga shekara ta 2015 ya zuwa har sau hudu.
Masu kyamar musulunci a kasar Jamus dai suna yin barazana ne ga masallatai da kuma cibiyoyin msulunci da suke cikin yankuna daban-daban na kasar.