IQNA

Wata Jaridar Najeriya Ta Yi Rubutu Kan Taron Arbaeen

23:35 - November 11, 2017
Lambar Labari: 3482090
Bangaren kasa da kasa, wata jaridar Najeriya People's Daily ta rubuta rahoto a kan taron Arbaeen da aka gudanar a Karbal.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na cibiyar yada al'adun musulunci cewa, jaridar Peoples Daily da ake bugawa a Najeriya ta rubuta rahoto a kan taron Arbaeen da aka gudanar a Karbala na kasar Iraki.

Jaridar ta ce wannan taron shi ne taron addini mafi girma da ake gudanarwa a duniya, wanda miliyoyin musulmi mabiya mazhabar shi'ar ahlul bait (AS) suke gudanarwa a kasar Iraki.

Wannan taron ya samo asali ne tun bayan waki'ar Ashura, inda aka kasha Imam Hussain (AS) tare da zuriyar manzon Allah da suke tare a Karbala, inda ake tunawa da abin da ya faru da kuma yin alhini kan hakan.

Tun bayan lokacin da Saddam Hussain ya kwace iko a kasar Iraki, ya hana gudanar da irin wadannan taruka na tunawa da zaluncin da aka yi wa iyalan manzon Allah a bayansa, amma bayan kawar da shi daga mulki, an ci gaba da gudanar da tarukan.

3662129


captcha