IQNA

Babban Masallacin Paris Ya Fice Daga Kwamitin Addinai Na Faransa

22:17 - January 05, 2018
Lambar Labari: 3482270
Bangaren kasa da kasa, babban masallacin birnin Paris na kasar Faransa ya fice daga kwamitin kasa na mabiya addinai sakamakon kin gayyatar babban daraktan masallacin a taron sabuwar shekara.

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin Russia Today cewa, bisa ga al’ada a kowace sabuwar shekara ana gayyatar shugabannin mabiya addinai a taron addu’ar sabuwar shekara wanda ake gudanarwa a fadar shugaban kasa da ke birnin Paris.

A karon farko cikin shekaru 25 a jiya an gudanar da irin wannan taro ba tare da an gayyaci babban daraktan masallacin Paris ba, wanda shi ne yake a matsayin wakilin musulmi a dukkanin lamurra da suka shafi gwamnati.

Masallacin Paris ya fitar da sanarwa da ke cewa, sakamakon rashin gayyatar Dalil Abubakar a wajen taron addu’a sabuwar shekara, kwamitin masallacin ya yanke shawar dakatar da halartar tarukan kwamitin addinai na kasar Faransa, kamar yadda kuma zai dakatar da halartar duk wasu taruka na gwamnatin kasa har sai abin da hali ya yi.

3679217

 

 

 

 

captcha