IQNA

Mai Shigar Da Kara A Kotun ICC Ta Bukaci A Yi Bincike Kan Kisan Rohingya A Myanmar

23:50 - April 10, 2018
Lambar Labari: 3482558
Bangaren kasa da kasa, Babbar mai shigar da kara a gaban kotun hukunta manyan laifuka ta duniya Fatou Bensouda, ta bukaci a gudanar da bincike kan kisan kiyashin da aka yi wa 'yan kabilar Rohingya a kasar Myanmar.

 

Kamfanin dillancin labaran iqn aya habarta cewa, Fatou Bensouda ta bukaci manyan alkalan kotun manyan laifuka ta duniya da su bayar da dama a gudanar da bincike kan kisan kare dangin da ake zargin an yi kan 'yan kabilar Rohingya a Myanmar.

Ta ce akwai batun da ake kan cewa kasar Bangaladesh ita ce mamba a kotun ICC, amma Myanmar ba mamba ce ba, wata kila hakan ya kawo tarnaki ga duk wani bincike da za a gudanar kan hakan, ta ce a ganinta wannan ba zai saba wa ko daya daga cikin dokokin kutun duniya ba.

Kungiyoyin kare hakkin bil adama na duniya da kuma masu sanya ido daga kasashen duniya daban-daban, sun bayyana kisan gillar da aka yi wa musulmi 'yan kabilar Rohingya a cikin kasa da shekara guda da ta gabata cewa, yunkurin share kabilar ne baki daya daga doron kasa, kuma dole ne kotun manyan laifuka ta duniya ta hukunta manyan jami'an sojin Myanmar da shugabannin addini Buda na kasar a  kan hakan.

3704482

 

 

 

 

 

captcha