Kamfanin dillancin labaran anatoly ya bayar da rahotn cewa, sakamkon kisan kiyashin da haramtacciyar kasar Isra’ila take yi kan Falastinawa a zanga-zanga mai taken hakkin komawa gida, mutane 132 ne suka yi shahada a yankin zirin Gaza da sauran yankuna.
Haramtacciyar gwamnatin yahudawan tana yin amfani da wannan damar wajen kashewa tare da jikkata dubban falastinawa a Gaza da sauran yankuna.
A jiya Juma’a wani matashi dan shekaru ashirin da tara ya yi shahada a Gaza, bayan da sojojin yahudawan sahyuniya suka harbe shi.