IQNA

Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama Na Duniya Bukaci Isra'ila Ta Saki Jarrar

23:54 - June 29, 2018
Lambar Labari: 3482797
Bangaren kasa da kasa, kungiyoyin kare hakkin bil adama na kasashen larabawa da wasu kasashen duniya sun bukaci Isra'ila ta saki Khalida Jarrar da ake tsare da ita.

 

Kamfanin dillancin labaran iqn aya habarta cewa, shafin yada labarai na kare hakkin falastinawa da Isra'ila take tsare da ya sanar da cewa, kungiyoyin kare hakkin bil adama na kasashen larabawa da wasu kasashen duniya sun bukaci Isra'ila ta saki Khalida Jarrar 'yar majalisar dokokin Palastine da ake tsare da ita tun shekarar da ta gabata.

Sharlut Kibs mai tuntuba na kunyar  ya bayyana cewa, suna cikin tuntubar kungiyoyin kare hakkin bil adama na duniya kan batun tsare falastinawa ba bisa kaida da Isra'ila ke yi, kuma duk suna nuna shirinsu na tunkarar wannan zalunci.

Khalida Jarrar tana tsare ne tun a cikin watan Yunin shekarar da ta gabata, Isra'ila takame ta ne saboda nuna rashin amincewa da cin zarafin falastinawa da suke tsare a gidajen kason Isra'ila.

3726214

 

 

 

captcha