Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a yau , daruruwan yahudawan sahyuniya masu tsatsauran ra'ayi sun kutsa kai a cikin masallacin quds mai alfarma tare da cikakkiyar kariya daga jami'an tsaron haramtacciyar kasar Isra'ila.
Wannan mataki dai yana zuwa ne bayan wani kutse da yahudawan suka yi a makon da ya gabata, inda suka shiga cikin harabar masallacin tare da keta alfarmarsa.
A yau ma yahudawan sun shiga har cikin ginin masallacin mai afarma, wanda hakan yana a matsayin wani mataki ne na tsokanar musulmi mazauan birnin.
Yahudawan Isra'ila dai sun jima suna aikata irin wannan danyen aiki, insda matasan palastinawa kan tare gabansu, amma a halin yanzu suna keta alfarmar masalalcin ne a hukumance tare da kariya daga gwamnatin yahudawa.