IQNA

21:57 - July 16, 2019
Lambar Labari: 3483847

Martanin Musulmi Ga Dan Takarar Kujerar Firayi Ministan Birtaniya

Dan takarar neman kujerar Firaim ministan kasar Britania ya bayyana kiyayyarsa ga addinin musulunci a wata hira da ta hada shi da jiridar Guardina ta kasar Britania.

Martanin Musulmi Ga Dan Takarar Kujerar Firayi Ministan Birtaniya

Kamfanin dillancin labaran iqna, jaridar ta Guardian ce ta bayyana haka a jiya Litinin, inda ta nakalto Boris Jonson yana fadar cewa addinin musulunci, addinin koma baya ne ga ga al-ummar duniya.

Amma kamfanin Tell MAMA wanda yake aikin lissafa mizanin kiyayyar da musulmim suke fuskanta a kasar Britania, ya bayyana cewa maganganun na Boris Jonson sun nuna cewa ya jahilci addinin musulunci.

Banda haka wasu rahotannin sun bayyana cewa kashi 52% na yan majalisar dokokin kasar Britania sun jahilcin matsayin da addinin musulunci ya ke da shi a tarihin bil’adama.

Kafin furucinsa na bayan bayan nan dai, Boris Jonson ya taba sifanta mata musulmi masu sanya hajibi a matsayin barayin banki.

Masana suna ganin da alamun idan Jonson ya haye kan kujerar Firai ministan kasar Biritania, yana iya kara takurawa musulman kasar.

3827562

 

 

captcha