Kamfanindillancin labaran iqna, Ahmad Taufiq ministan ma’aikatar kula da harkokin addini a kasar Morocco ya bayyana cewa, lokacin malidin manzon Allah (SAW) lokaci ne na raya dukkaninayyuka da ya koyar da al’ummar musulmi.
Ya ci gaba da cewa, daya daga cikin hanyoyin raya ranakun maulidin manzon Allah ita ce karatun kur’ani, da kuma tunatarwa kan darussan da suke cikin rayuwarsa mai albarka.
Ya kara da cewa an kafa kwamiti na malamai wanda yake kula da dukkanin abubuwan da ake gunaraa na fadakarwa da kuma bayanai kan tarihin manzo da wajacin koyi da shi a cikin dukkanin abubuwan da ya oyar da al’ummar musulmi.