Kamfanin dillancin labaran IQNA, shafin yada labarai na sadal balad ya habarta cewa, Sabri Ibadah mataimain ministan harkokin addini ya bayyana cewa a jiya an gayyaci limamin wani masallaci da ya fassara ayoyin kur’ani bisa kure a Masar a garin Tanta da ke cikin lardin Garbiyya a kasar.
Wannan mataki dai yana zuwa ne bayan da limamin ya fassara wasu ayoyin kur’ani a cikin hudubar juma’a bisa kure, wanda hakan ya dauki hankulan jama’a.
An nada wannan limami ne dai tun a kimanin shekaru ashirin da suka gabata, inda kuma yake gabar da huduba a kowace Juma’a, wanda hakan yasa cibiyar azhar ta nuna takaicinta da faruwar hakan.