IQNA

“Kahira Da Bukhara” Biranan Ilimi Da Al’adun Musulunci Na 2020

15:23 - December 18, 2019
Lambar Labari: 3484329
Cibiyar ISESCO ta zabi biranan Kahira da Bukhara a mtsayin biranan al’adun musulunci na 2020.

Kamfanin dillancin labaran IQNA, cibiyar bunkasa ilimi da al’adun mulsunci ta duniya ISESCO ta zabi birnin Tunis a matsayin birnin al’adu na 2019, sai kuma biranan Kahira da Bukhara a mtsayin biranan al’adun musulunci na 2020 mai zuwa.

Salem bin Muhammad Almalik shugaban cibiyar ta ISESCO ya bayyana cewa, manufar hakan ita ce kara bunkasa al’adun muslunci.

Ya e an zabi birnin Tunis ne saboda irin tsohon tarihin da yake da shi na ilimi da kuma yada al’adu na addinin muslunci, wanda hatta Ibn Khaldun daya daga cikin manyan malaman addinin muslunci da suka yi rubuce-rubece, ya rayu ne a wannan birnin.

Muhammad Zainul abiding ministan yada al’adu na Tunisia yay aba da yadda taron ya gudana cikin nasara.

3865054

 

captcha