Kamfanin dillancin labaran IQNA, ma’aikatar watsa labarai ta Palestine ta bayar da bayanin cewa, ‘yan jarida maza 237 da kuma ‘yan jarida mata 71 ne jami’an tsaron Isra’ila suka ci zarafinsu a cikin shekarar da ta gabata.
Baya ga haka kuma, a cewar bayanin na ma’aikatar watsa labaran Palestine, a cikin shekarar da ta gabata Isra’ila ta rufe shafukan yanar gizo guda 160 na kafofin yada labarai.
Kamar yadda kuma mafi yawan ‘yan jaridar da aka ci zarafinsu suna cikin gudanar da aikinsu ne, musamamn ma masu bayar da rahotannia zanga-zanga da gangamin mutanen Gaza, inda ‘yan jarida da dama suka samu munanan raunuka.
https://iqna.ir/fa/news/3871535