Karamini ofishin jakadancin Iran a kasar Tunisia ya sanar da cewa, an bude kofar gudnar da gasar rubutun makalaloli mai taken Quds a mahangar masana a kasar tun daga wannan mako, domin bayar da dama gam asana su bayyana mahangarsu kan batun Quds, wanda hakan ya zo ne a daidai lokacin da aka sanar da dae tarukan ranar Quds a wannan shekara.
Bayan kammala amsar makalolin da aka rubuta za a bayyana wadanda suka zo na daya da na biyu da kuma na uku, haka nan kuma za bayar da kyautuka na musamman ga dukkanin wadanda aka zabi makalolinsu.