IQNA

16:16 - May 08, 2020
Lambar Labari: 3484775

Wani Jami’in Gwamnatin Sudan Ya Yi Batunci Ga Addini

Tehran (IQNA) daraktan cibiyar tsara manhajar karatu ta kasa a Sudan ya bukaci da a cire kur’ani daga cikin manhajar karatu a makarantun share fagen shiga firamare.

Wani Jami’in Gwamnatin Sudan Ya Yi Batunci Ga Addini

Shafin yada labarai na almustaqbal ya bayar da rahoton cewa, Umar Ahmad Alqarai Babban daraktan cibiyar tsare-tsaren manhajar karatu da kuma kula da ayyukan madaba’antu a Sudan, ya mika bukatarsa ta neman a cire kur’ani daga cikin manhajar karatu a makarantun share fagen shiga firamare a fadin kasar Sudan, bisa hujjar cewa koyar da wasu abubuwa da ke cikin kur’ani ga kananan yara yana tattare da hadari.

Wannan lamari ya fuskanci kakkausan martani daga ko’ina  a cikin fadin kasar ta Sudan, tare da bayyana wannan furuci da cewa yana a matsayin batunci ga kur’ani mai tsarki da ma addinin muslunci baki daya.

A kan haka jama’a suna ci gaba da yin kira ga sabbin mahukuntan kasar ta Sudan da su gaggauta daukar matakin tsige wannan jami’i daga kan mukaminsa, sannan kuma a hukunta shi a kan kalaman da ya furta dangane da kur’ani mai tsarki.

 

3897207

 

 

 

 

captcha