
A wata zantawa da ya yi da shafin yada labarai na sadal balad sheikh Hani Alhusaini ya bayyana cewa, ya hardace kur’ani mai tsarki ne tun yana dan shekaru 19 da haihuwa.
Ya ci gaba da cewa, a cikin shekara ta 2020 ne aka dauke shi a matsayin mai karatu a hukumance a gidan radiyo da talabijin na kasar Masar, kuma tun daga lokacin ne ya fara halartar manyan tarukan karatun kur’ania kasashen duniya.
Ya ce ya samu tarbiya ne tun daga gidansua gaban mahaifansa, bayan nan kuma ya samu wata tarbiyar da karatua gaban manyan malamansa da suka hada da sheikh Abul Ainain Shu’aisha.
Bayan nan kuma ya ci gab ada harkokinsa na koyar da dalibaia makarantu daban-daban a cikin kasar ta Masar, domin samun albarkar kur’ani mai girma ta hanyar koyar da wasu abin da ke cikinsa.
Ya kara da cewa, ya kasance mai shaukin kur’ani tun yana karami, kuma Allah ya albarkaci rayuwarsa da karatunsa da kuma hardarsa, tare das aka dukkanin lokacinsa a cikin lamarin kur’ani.