IQNA

16:34 - August 07, 2020
Lambar Labari: 3485063

Sayyid Hassan Nasrullah Zai Gabatar Da Wani Jawabi

Tehran (IQNA) Babban sakataren kungiyar Hizbullah a kasar Lebanonzai gabatar da wani jawabi dangane da halin da ake ciki a kasar da yankin.

Sayyid Hassan Nasrullah Zai Gabatar Da Wani Jawabi

Shafin alahad ya bayar da rahoton cewa, da yammacin yau Babban sakataren kungiyar Hizbullah Sayyid Hassan Nasrullah zai gabatar da jawabi a yau wanda zai fara daga misalin karfe 17:30 na yamma agogon birnin Beirut.

A cikin jawabin nasa ana sa ran Sayyid Nasrullah zai tabo muhimman lamurra ne dangane da abin da ya shafi hatsarin da auku a birnin Beirut, da kuma matsayar Hizbullah kan hakan, da ma sauran lamurra da suka shafi yankin gabas ta tsakiya.

3915152

 

captcha