IQNA

An bayar Da Sanarwar Bude masallatai Domin Salloli Biyar A Rana A Lagos

22:38 - September 20, 2020
Lambar Labari: 3485202
Tehran (IQNA) gwamnatin jihar Lagos a Najeriya ta bayar da sanarwar cewa, za a iya bude masallatai domin gudanar da salloli biyar na kowace raa, amma bisa sharadin kiyaye dukkanin ka’idojoji na kiwon lafiya.

Gwamnatin jihar Lagos ta bayyana cewa, majami’un kiristoci da ke jihar za su iya ci gaba da gudanar da harkokinsu na ibada, amma dole a kiyaye ka’idojin da aka gindaya, da suka hada da wanke hannuwa da fesa maganin kashe kwayoyin cuta da kuma bayar da tazara.

Dangane da gidajen silima kuwa, gwamnatin Lagos ta bayyana cewa za a iya bude kashi talatin cikin dari ne kawai.

Najeriya dai na daga cikin kasashen Afirka da suka bayyana cewa suna daukar matakan da suka dace wajen dakile yaduwar cutar, wanda hakan yasa cutar ba ta yi tasiri ba kamar wasu kasashen, duk kuwa da yawan jama’a da ke akwai a kasar.

 

 

3923975

 

 

 

 

 

 

captcha