A cikin wani bayani da ya fito daga ma’aikatar harkokin wajen Iran, an bayyana cewa a kokarin da kasar take yi domin sasanta kasashen Azarbaijan da kuma Armenia a rikicin da ya kunno kai a tsakaninsu,a daren jiya Litinin, ministan harkokin wajen Iran ya zanta da jami’an gwamnatocin kasashen biyu.
Muhammad Jawad Zarif ya zanta ministocin harkokin wajen kasashen Azarbaijan da kuma Armenia a lokuta daban-daban a daren jiya, inda yake kokarin ganin an samu sulhu da fahimtar juna, domin kawo karshen tayar da jijiyoyin wuya a tsakanin kasashensu.
Iran ta bayyana kasashen biyu a matsyin makwabtanta, wadanda zaman lafiyarsu zaman lafiyarta ne, a kan haka za ta ci gaba da yin kokari domin sulhunta su.
3925813