IQNA

Zarif Ya Tattauna Da Ministocin Harkokin Wajen Azerbaijan Da Armenia Domin Sulhunta Su

19:51 - September 28, 2020
Lambar Labari: 3485227
Tehran (IQNA) Iran ta sanar da cewa tana kokarin shiga tsakanin kasashen Azarbaijan da kuma Armenia domin sasanta su kan rikicin da suke yi.

A cikin wani bayani da ya fito daga ma’aikatar harkokin wajen Iran, an bayyana cewa a kokarin da kasar take yi domin sasanta kasashen Azarbaijan da kuma Armenia a rikicin da ya kunno kai a tsakaninsu,a  daren jiya Litinin, ministan harkokin wajen Iran ya zanta da jami’an gwamnatocin kasashen biyu.

Muhammad Jawad Zarif ya zanta ministocin harkokin wajen kasashen Azarbaijan da kuma Armenia a lokuta daban-daban a daren jiya, inda yake kokarin ganin an samu sulhu da fahimtar juna, domin kawo karshen tayar da jijiyoyin wuya a tsakanin kasashensu.

Iran ta bayyana kasashen biyu a matsyin makwabtanta, wadanda zaman lafiyarsu zaman lafiyarta ne, a kan haka za ta ci gaba da yin kokari domin sulhunta su.

 

3925813

 

captcha