IQNA

Iran Ta Mayar Wa Saudiyya Da Martani Kan Zargin Da Ta Yi Mata

23:11 - September 29, 2020
Lambar Labari: 3485229
Tehran (IQNA) mayar da martani dangane da zargin da Saudiyya ta yi na cewa sun kama wasu mutane da suka kira ‘yan ta’adda da suka ce suna da alaka da Iran.

Kakakin ma’ikatar harkokin wajen kasar Iran Saeed Khatibzadeh ya bayyana cewa, zargin da mahukuntan Saudiyya suka yi ba sabon lamari ba ne, maimaici ne, kuma zai fi kyau ga mahukunatn na masarautar Al Saud da su zabi hanyar bin gaskiya da yin amfani da hikima domin kare mutuncinsu.

Ya ce ko lokutan baya sun zargi wasu da suka danganta su da ayyukan ta’addanci saboda ra’ayoyinsu an siyasa, ko kuma saboda banbancin akida, wanda hakan ba daidai ba ne.

Khatibzadeh ya ce a kokarin da mahukuntan Saudiyya suke yi domin neman burge iyayen gidansu, suna kirkirar karya tare da danganta ta da kasar Iran, kuma su cutar da mutanen kasarsu da ke adawa ta siyasa a kan tsarin kama karya na kasar, ta hanyar danganta su da ayyukan ta’addanci.

Ya ce irin wadannan makirce-makirce ba za su iya cutar da Iran ba, domin kuwa ta saba da su tsawon shekaru daga iyayen gidan sarakunan Saudiyya.

Bayanin nasa ya kara da cewa, a duniya kowa ya san inda cibiyar akidar ta'addanci da sunan addini  take, inda kungiyoyin 'yan ta'adda na alqaeda da IS da makamantansu suke samo tunanin tsatsauran ra'ayi na ta'adanci, da kafirta musulmi.

3926193

 

 

Abubuwan Da Ya Shafa: mahukuntan Saudiyya
captcha