Majiyar fadar sarkin kuwait ta bada sanarwan cewa Sarki Sheikh Sabah Al-Ahmad Al-Jabir Assabah ya rasu yana dan kimanin shekaru 91 a duniya.
Rahotanni daga kasar ta Kuwait sun bayyana cewa sarkin ya dan dade yana fama da rashin lafiya. Har yanzun dai ana jiran Karin bayani dangane da rasuwar sarkin.
Har’ila yau a wani Labarin kuma gwamnatin kasar Kuwait ta ki amincewa da shugabancin kungiyar kasashen Larabawa karo na dari da biyar bayan da gwamnatin Falasdinawa a Ramallah ta ki amincewa da shugabancin.
Kafin haka dai a ranar Talatan da ta gabata ce gwamnatin Falasdinawa a Ramallah ta ki amincewa da karbi shugabancin karba-karba na kungiyar kasashen Larabawan, saboda maida huldar jakadancin da kasashen Bahrai da Hadaddiyar daular larabawa suka yi da kuma goyon bayan da kungiyar ta nuna dangane da hakan.
A ranar sha biyar ga watan Satumban da muke ciki ne kasashen biyu suka rattaba hannun kan yarejejeniyar maida huldar jakadanci da Isra’ila a fadar shugaban kasar Amurka.
3926288