IQNA

An Ji Kalmar Insha Allah A Muhawara Tsakanin Trump Da Biden

23:23 - September 30, 2020
Lambar Labari: 3485233
Tehran (IQNA) an tafka muhawara tsakanin shugaban kasar Amurka da kuma dan takarar shugabancin kasar karkashin inuwar jam’iyyar democrat.

Muhawarar wadda aka tafka tsawon mintuna casa'in wadda kuma aka watsa kai tsaye a kafofin yada labarai na Amurka da ma na duniya, ta nuna yadda mutanen biyu suka yi ta sukar junansu da kuma fallasa kansu.

A bisa ga yadda muhawarar ta gudana, Trump ya kasance a mai kare kansa ne bisa tuhumce-tuhumce a mafi yawan lokacin muhawarar, yayin da shi kuma Biden ya kasance mai kai farmaki a kan Trump.

Wasu sun yi la'akari da cewa a cikin kalamansa Joe Biden ya yi amfani da kalmar "Insha'allah" wato kalmar ad musulmi suke fadia  cikin zantukansu.

Biden ya bayyana Trump a matsayin wanda ya kara ruruta wutar rikicin wariyar launin fata da ake nuna ma bakaken fata akasar Amurka, inda Trump ya rika sukar masu zanga-zanga tare da kiransu a matsayin ‘yan daba ‘yan ta’adda, yayin da shi kuma Trump ya kare kansa da cewa, zanga-zangar ba ta zaman lafiya ba ce.

3926400

 

captcha