IQNA

An Saka Tulluwar Masallacin Qaitabai A Cikin Muhimman Wuraren Tarihi A Masar

17:00 - March 31, 2021
Lambar Labari: 3485773
Tehran (IQNA) ma’aikatar kula da harkokin al’adu da tarihi ta kasar Masar ta sanar da saka tulluwar masallacin Qaitabai a cikin wuraren tarihi.

Shafin yada labarai na jaridar Egypt Today ya bayar da rahoton cewa, ma’aikatar kula da harkokin al’adu da tarihi ta kasar Masar ta sanar da saka tulluwar masallacin Qaitabai a cikin wuraren tarihi na kasar.

Wannan masallaci tarihinsa na komawa zuwa ga lokacin mulkin sarakunan Qaitabai a kasar Masar, a kan haka aka saka shi cikin muhimman wurare na tarihi.

An gina wannan wuri ne a cikin shekara ta 866 zuwa 899 hijira kamariyya, sannan kuma an saka wasu duwatsu biyu a wurin wadanda wani mutum ya zo da su daga Hijaz, kuma ake danganta su da manzon Allah (SAW) insda sarki Qaitabai ya sayi duwatsun biyu kuma ya bayar da umarni aka saka su a wannan masallaci.

Amma bayan da sarakunan daular Usmaniya suka mamaye Masar, sai suka dauke wadannan duwatsu suka tafi da su zuwa Istanbul, inda aka saka sua  masallacin Sultan Ahmad, amma daga bisani wani daga cikin sarakunan daular Usmaniya ya bayar da umarni aka mayar da su zuwa Hijaz a wurinsu an asali.

3961821

 

 

 

 

captcha