IQNA

Kungiyoyin Jin Kai Na Tallafa Wa Marassa Galihu A Aljeriya A Cikin Watan Ramadan

22:43 - April 19, 2021
Lambar Labari: 3485827
Tehran (IQNA) Kungiyoyin jin kai da dama ne suke gudanar da ayyukan tallafa wa marassa galihu a kasar Aljeriya a cikin watan Raadan mai alfarma.

Tashar Sky News Arabic ta bayar da rahoton cewa, daruruwan kungiyoyin jin kai a kasar Aljeriya suna gudanar da ayyukan taimakon marassa karfi, tare da tallafa musu a cikin watan Ramadan.

Rahoton ya ce, wadannan kungiyoyi akasarinsu kungiyoyi ne na matasa, wadanda suna gudanar da irin wadannan ayyuka a sauran lokuta na shekara, amma suna rubanya ayyukan nasu a cikin watan Ramadan.

Daga cikin ayyukan nasu hard a shirya buda baki tare da gayyatar mutane musamman marassa galihu domin su ci abincin da aka tanada, amma a wannan karon saboda kaucewa yaduwar cutar corona, suna gudanar da ayyukan nasu ne ta hanyar tanadar abinci, da kuma rarraba shi ma mutane gida-gida.

Haka nan kuam sukan raba abincin ga mutane masu wucewa a kan tituna, musamman wanda suka fahimci yana cikin bukata.

Wadannan matasa dai suna gudanar da wannan aikin ne ta hanyar tattara abin da suke samu a  wuraren ayyukansu, tare da yin sadaukarwa da shi ga mabukata.

3965673

 

captcha