Taron mai taken "Haɗin kan Al'ummar Manzon Allah (SAW) ya gudana ne a yankin Kashmir tare da halartar gungun malaman Shi'a da Sunna.
A ranar Laraba da t gabata ce 4 ga watan Nuwamba aka gudanar da taron hadin kan al'ummar manzon Allah (SAW) a yankin Shalimar na Srinagar da ke Kashmir.
Majalisar Malamai ta yankin Kashmir ce ta dauki nauyin gudanar da taron, inda aka kammala da addu’ar samun hadin kai al'ummar musulmi baki daya.