IQNA

Jordan Ta Yi Allawadai Da Kalaman Isla'ila Dangane Da Masallacin Quds

21:08 - November 30, 2021
Lambar Labari: 3486625
Jordan Ta Yi Allawadai Da Kalaman Isla'ila Dangane Da Masallacin Quds
Tehran (IQNA) gwamnatin kasar Jordan ta yi Allawadai da furucin gwamnatin Isra'ila na halasta gina wani wurin bautar yahudawa a cikin harabar masallacin Quds

Tahar TRT ta bayar da rahoton cewa, gwamnatin kasar Jordan ta yi Allawadai da furucin gwamnatin Isra'ila na halasta gina wani wurin bautar yahudawa a cikin harabar masallacin Quds mai alfarma.

A cikin wata sanarwa da kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Jordan Haitham Abu al-Faul ya fitar, ya bayyana kalaman na Isra'ila a matsayin tsokana da rashin hujja kan masallacin Al-Aqsa.
 
Abu al-Ful ya kara da cewa: Wadannan maganganu an yi Allah wadai da su, kuma an yi watsi da su, kuma ana daukar su a matsayin babban cin zarafi na tarihin masallacin Al-Aqsa.
 
Abu al-Ful ya jaddada cewa gaba dayan masallacin Al-Aqsa da farfajiyarsa na mallaki ne na al'ummar musulmi.
 
Ya yi nuni da cewa: Ofishin da ke bayar da kulawa ga ayyukan masallacin da ke birnin Kudus, da kuma kuma hukumar harkokin masallacin Al-Aqsa ta kasar Jordan wadda ita ce hukumar da bangarorin kasa da kasa suka mika wa lamarin kula da Quds a bisa tsari na majalisar dinkin duniya, duk wannan na tabbatar da cewa larabawa da musulmi suke da hurumin kula da masallacin ba yahudawa ba.

 

4017542

 

captcha