Tehran (IQNA) Al-Azhar ta yi gargadi kan sabbin dabarun kungiyoyin 'yan ta'adda, musamman ISIS, na kai hare-haren ta'addanci.

Shafin Alwafd ya bayar da rahoton cewa, Al-Azhar ta yi gargadin cewa kungiyoyin 'yan ta'adda, musamman ISIS, ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen yin amfani da na'urorin fasaha da fasahar zamani wajen aiwatar da makircinsu na ta'addanci da kutsawa yankuna daban-daban, musamman a nahiyar Turai.