A wani taron manema labarai na hadin gwiwa da ya yi da takwaransa na Tunisiya, Shugaban kasar Aljeriya Abdel Majid Taboun, ya jaddada wajabcin komawar Syria cikin kungiyar kasashen Larabawa, inda ya ce sake hadewar kasashen Larabawa na bukatar Syria ta koma cikin kungiyar kasashen Larabawa, domin a cewarsa babu wani babban bambanci tsakanin kasashen Larabawa.
Shugaban na Aljeriya ya kuma bayyana fatansa na cewa taron kungiyar kasashen Larabawa da za a yi a watan Maris zai dawo da daidaito a tsakaninsu da fahimtar juna.
Abdel Majid Taboun wanda ya ziyarci kasar Tunisia inda ya gana da shugaban kasar Qais Saeed, ya ce ya gamsu da shawarwarin shugaban kasar Tunusiya, kan yadda za a warware rikicin Libiya cikin lumana, da kuma cewa sojojin haya da sojojin kasashen waje dole ne su fice daga kasar ta Libya.
Tun a watan Nuwamban shekara ta 2011 ne aka dakatar da kasar Siriya a matsayin ta kungiyar kasashen Larabawa, sakamakon matsin lamba na wasu kasashen da suka mamaye kungiyar, kuma suke shimfida siyasarsu a kanta yadda suka ga dama.