Tehran (IQNA) Hukumar kula da masallatai masu tsarki guda biyu a kasar Saudiyya ta shirya wani baje koli domin fadakar da mahajjata fasahar saka labulen Ka'aba.

Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Sawa Al-Akhbariya cewa, hukumar kula da wuraren ibada guda biyu a kasar Saudiyya ta shirya wani baje koli domin fadakar da mahajjata sana’ar saka labulen Ka’aba a haramin Makkah.
A cikin wannan baje kolin, mahajjata sun koyi fasahar saka labule na Ka'aba, da zane-zane da hanyoyin saka kalmomi da ma'anonin sa, tare da gudanar da wani takaitaccen bangare na wannan fasaha a karon farko.





