Hojjat-ul-Islam wal-Muslimeen Sayyid Mohammad Zulfiqari, manajan bangaren kula da ayyukan maziyarta wadanda ba Iraniyawa ba, a wata hira da ya yi da IQNA ya bayyana cewa: Jagoran juyin juya halin Musulunci zai gabatar da jawabi a ranar farko ta sabuwar shekarar shamsiyya, ga masu ziyara a hubbaren Radhwi, za a fassara kalmominsa a lokaci guda, ana yin shi a cikin harsuna hudu na duniya.
Ya kara da cewa: Za a tura masu ziyara da ba na Iran ba ne zuwa mashigar Darul Rahmah da Ghadir domin sauraron jawabin Jagoran juyin juya halin Musulunci, sannan kuma za su saurari jawabin shugaban a daidai lokacin da sauran mazu ziyara Iraniyawa su ma suke sauare.
Hojjat-ul-Islam Zulfiqari ya bayyana cewa: Fassarar lokaci guda zuwa harsunan Ingilishi da Larabci da Azeri da Urdu karkashin taken "Daukakar Ziyara" masana sashen fassara za su yi.