IQNA

Bukatar Kungiyar Hadin Kan Musulunci daga Denmark:

Aiwatar da kudurin Majalisar Dinkin Duniya kan kiyayyar addini

16:06 - July 24, 2023
Lambar Labari: 3489529
Jeddah (IQNA) Kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta bukaci hukumomin kasar Denmark da su aiwatar da kudurin Majalisar Dinkin Duniya kan kyamar addini.

Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, wakilin kungiyar hadin kan musulmi a majalisar dinkin duniya ya fitar da sanarwar yin Allah wadai da wulakanci da kona kur’ani mai tsarki da ake yi a kasar Denmark tare da neman mahukuntan wannan kasa da su kiyaye hakkinsu kamar yadda dokokin kasa da kasa suka tanada.

A cikin wannan bayani da aka buga a shafin Twitter na wannan kungiya, an bayyana cewa: Muna yin Allah wadai da wulakanta kur’ani mai tsarki a kasar Denmark a kwanakin baya.

A cikin wannan bayani yana nanata cewa: Ci gaba da kare wadannan ayyuka na adawa da Musulunci da kuma rashin hana su bisa hujjar 'yancin fadin albarkacin baki, yana kara rura wutar rashin adalci a wannan fanni.

Wannan kungiya ta bukaci Denmark da ta cika nauyin da ya rataya a wuyanta bisa dokokin kasa da kasa da kuma aiwatar da kudurin kwamitin kare hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya kan kyamar addini.

Sanarwar ta ce: Wadanda ba su daga murya ba, duk da bayyanannun umarnin hukumar kare hakkin bil'adama, za su yi saurin rasa amincin su.

A ranar 12 ga watan Yuli ne hukumar kare hakkin bil adama ta Majalisar Dinkin Duniya da ke birnin Geneva ta yi Allah wadai da keta haddin kur'ani mai tsarki a karshen watan Yunin da ya gabata a kasar Sweden, duk da rashin amincewar da kasashen yammacin duniya suka yi kan kudurin da wannan majalisar ta gabatar.

Wannan kuduri ya bukaci yin Allah wadai da hare-haren da ake kaiwa kur'ani, kuma bisa wannan kuduri an bayyana irin wadannan ayyuka a matsayin kiyayya ta addini.

A ranar Juma'ar da ta gabata ne wata kungiyar masu adawa da Musulunci ta kasar Denmark ta kona kur'ani mai tsarki a gaban ofishin jakadancin Iraki da ke birnin Copenhagen.

 

4157417

 

captcha