IQNA

Wasu Musulmi Sun Gudanar Da Zama Kan Fadakar Musulmi A Najeriya

10:46 - May 21, 2014
Lambar Labari: 1409194
Bangaren kasa, a ci gaba da gudanar da taruka da ake yi a kasashen musulmi kan fadakar al’ummar a cikin wadannan shekaru a tarayyar Najeriya ma an gudanar da irin wannan zama tare da halartar wasu daga cikin musulmin kasar.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na MASFON cewa, an gudanar da zaman fadar musulmi a Najeriya tare da halartar wasu daga cikin musulmin kasar, wanda hakan y aba su damar tatatuna batutuwa da suka shafi matsalolin da musulmin kasar suke fuskanta.
Babbar matsalar da ake fuskanta ta fuskar tsaro dai a Najeriya it ace matsalar kungiyar Boko Haram, kungiyar da take da alaka da masu tsatsauran ra’ayin wahabiyanci da kafirta musulmi.
A cikin lokutannan kungiyar ta kaddamar da hare-haren ta’addanci a cikin sassan kasar wanda hakan yay i sanadiyyar mutuwar mutane da dama akasarin wadanda kungiyar take kaiwa hare-hare kuwa musulmi ne mazauna yankunan arewacin kasar kasar.

1408936

Abubuwan Da Ya Shafa: najeriya
captcha