IQNA

Musulmin Kenya Sun Nuna Rashin Amincewa Da Batun Hana Hijabi Ga Dalibai

23:02 - September 30, 2014
Lambar Labari: 1455974
Bangaren kasa da kasa, musulmin kasar Kenya sun nuna rashin amincewarsu da batun wata doka da majalisar dokokin kasar ke bahasi kanta da ke neman haramta wa 'yan mata musulmi saka hijabin muslunci a makaranta.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na On Islam cewa, kungiyoyin musulmin kasar Kenya sun nuna rashin amincewarsu da batun wata doka da majalisar dokokin kasar ke bahasi kanta da ke neman haramta wa 'yan mata musulmi saka hijabin muslunci a makarantun boko a kasar.

Shugaban kungiyar musulmin kasar Kenya Abdulalh Godou ya bayyana cewa, za su dauki dukkanin matakan das ka dace domin dakile wannan yunkuri wanda ya sabawa dukaknin dokokin kasar na bayar da 'yancin gudanar da ayyukan addini ga dukaknin 'yan kasa ba tare da nuna wani bambanci ko takurawa ba, wanda kuma yin hakan takura ma musulmi ne bisa addininsu.

Ya kara da cewa bisa dokoki da kaidoji na addinin muslunci a duk lokacin da diya mace ta isa shekarun balaga, to daga lokacin ya zama wajibia  kanta a cikin muslunci da ta rika rufe jikinta daga sauran mutane wadanda ba muharramanta ba, kuma tilasta yan mata musulmi das u daina saka hijabia  makarantun tamkar cin zarafi ne a gare su.

Kasar Kenya dai tana da mutane da suka kai miliyan 36 miliyan 10 kuma mabiya  addinin muslunci ne.

1455118

Abubuwan Da Ya Shafa: kenya
captcha