IQNA

15:29 - March 10, 2009
Lambar Labari: 1754367

Hanyar Fuskantar Ma'abuta Girman kai Na Duniya Hadin Kai Tsakanin Kasashen Musulmi

Bangaren siyasa: shugaban majalisar fayyace tsarin musulunci a Iran ne ya bayyana cewa : kasashen musulmi da masu tasowa su hada kansu idan suna son fuskantar ma'abuta girman kai na duniya day an mulkin mallaka.

Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a Iran Ikna ce ta nakalto daga ofishin hulda da jama'a na majalisar fayyace tsarin musulunci a Iran ce Ayatullahi Hashimi Rafsanjani a lokacin ganawarsa da shugaban majalisar dokokin Mali ya bayyana masa cewa: kasashen Iran da mali sun fadada dangantakarsu da huldar kasashen biyu kuma kasashen musulmi da sauran takwarorinsu masu tasowa na iyan samun ci gaba ta hanyar hada kai kuma ta wannan hanya ce za su fuskanci kasashe ma'abuta girman kai da danniya a duniya . A yau siyasar duniya na bukatar kasashen musulmi da su hada kansu domin kubutar da al'ummominsu daga zaluncin manyan kasashe.

375217
captcha