Daga Jodan ne cibiyar da ke kula da harkokin Kur'ani a Iran Ikna ce ta bayyana cewa: Jaridar Algad ta kasar ta jodan ta jiyo Hamza Mansur shugaban jabahatul Amal islami a wannan kasa yana cewa: hukumcin fitar da sammacin kama shugaban kasar Sudan Umar Albashir da kotun duniya mai tuhumar manyan leifuka ta yi ya karawa shugaban na Sudan farin jini a idon duniya kuma ya karawa duniyar musulmi kusanci da fahimtar juna a daidai wannan lokaci na zalumci da nuna wariya a fili karara.Mansuri ya kara bayyana cewa: wannan hukumci ba komi ban e face kara nuna wariya a kan musulmi da larabawa kuma za su ci gaba da adawa da wannan hukumci.
380264