Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga jaridar shar al-ausat cewa; An fara gudanar da zaman tattaunawa na kasa da kasa tsakanin mabiya addinai daban-daban a birnin Vienna fadar mulkin kasar Austaria, wanda yake samun halartar masana da kuma malaman addinai daban-daban. Bayanin ya ci gaba da cewa wannan taro nana gudanar da shi ne a matsayin ci gaba da taron nan da aka fara gudanarwa a birnin Washington da kuma Madrid, wanda sarkin kasar saudiyya Abdullah Bin Abdulaziz ya bayar da shawarar gudanar da shi. A lokacin bude zaman taron Abdullah bin Muhsin Al-turaiki ya bayyana cewa, babbar manufar gudanar da taron dai ita ce samun fahimtar juna tsakanin mabiya addinai, da kuma yi wa kowane daya bangare adalci maimakon kyamar juna.
433767