Kamfanin dillancin labaran ikna ya nakalto daga bangaren yada labaransa na kasar Malazia cewa; Kasashe 47 ne na duniya suke halartar taron gasar karatu da harder kur'ani mai tsarki a birnin Kualalampur na kasar Malazia, inda yanzu haka ake ci gaba da gudanar da wannan gasa kamar yadda aka shirya ta. Bayanin ya ci gaba da cewa gasar karatun kur'anin tana samun ci gaba fiye da sauran lokutan da suka gabata idan aka kwatanta da sauran lokutan da aka gudanar da wannan gasar.
444570