Cibiyar da ke kula da harkokin addini a Iran a reshenta da ke hukumar da ke kula da yada al'adun Iran ta watsa rahoton cewa: an gudanar da bincike da nazari kan wajibcin kare muhalli da tsabtace shi a mahangar addinin Musulunci da kuma addinai a kasar Indiya. Kuma burin gudanar da wannan taro shi ne bayani kan addinin Musulunci a matsayinsa na addinin zaman lafiya da sulhu da kuma a dabra da haka a gudanar da irin wannan bincike a cikin addinin Musulunci da addinai a kasar Indiya. Kuma a gurin wannan taro an samu halartar wakilai masu yawa da kuma shugabannin jami'o'i.
550994