Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, majalisar dokokin palastinu ta fitar da wani bayani da a cikinsa take yin Allawadai da matakin da yahudawan sahyuniya suka dauka fitar da wasu dubbai daga yankunan gabar yamma da kogin Jordan. Bayanin ya ci gaba da cewa yanzu haka yahudawan sun fara aiwatar da wannan shiri nasu, kuma abin da suke son yi shi ne korar dukkanin palastinawa ba wasu dubbai ba kawai. 561291