IQNA

Taron share Fage Na Kasashen Musulmi Kan Kare Hakkin Yara Kanana

15:16 - May 02, 2010
Lambar Labari: 1916137
Bangaren kasa da kasa: a birnin Trablus fadar mulkin kasar Libya ne za a gudanar da taron share fagen taron ma'aikatun cikin gida na kasashen musulmi da zai tattauna kan kare hakkin kananan yara daga ranar sha uku zuwa sha hudu ga watan Ordebehesht na shekara ta dubu daya da dari uku da tamanin da tara.
Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran Ikna bayan ta nakalto daga majiyar labarai ta Isesco ta watsa rahoton cewa: a birnin Trablus fadar mulkin kasar Libya ne za a gudanar da taron share fagen taron ma'aikatun cikin gida na kasashen musulmi da zai tattauna kan kare hakkin kananan yara daga ranar sha uku zuwa sha hudu ga watan Ordebehesht na shekara ta dubu daya da dari uku da tamanin da tara. A lokacin wannan taro mahalarta za su yi nazari da bincike kan abubuwan da suka shafi matsalolin da ke addabar yara kanana.


571243
captcha