Bangaren kasa da kasa; malamai musulmi da suka halarci taron limamai da malama daga kasashen kungiyar Balkan a ranar alhamis din da ta gabata ashirin da uku ga watan Ordebehesht na shekara ta dubu daya da dari uku da tamanin hijira shamsiya a cikin wani bayani da suka fitar sun bukaci musulman yankin da su hada kansu da zama tsintsiya guda.
Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran ikna bayan ta nakalto daga beyazgazete ta watsa rahoton cewa; ; malamai musulmi da suka halarci taron limamai da malama daga kasashen kungiyar Balkan a ranar alhamis din da ta gabata ashirin da uku ga watan Ordebehesht na shekara ta dubu daya da dari uku da tamanin hijira shamsiya a cikin wani bayani da suka fitar sun bukaci musulman yankin da su hada kansu da zama tsintsiya guda. Mahalarta taron sun yi bayani dalla-dalla kan muhimmancin hadin kai da kuma irin nasarorin da ke biyo bayansa da kuma musamman a wannan lokaci da musulmi ke fuskantar babban kalubale.
579072