Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran ikna bayan ta nakalto daga majiyar watsa labarai ta Nasij ta watsa rahoton cewa; Arik Huldar babban alkali a kotun koli ta Amerika ya bukaci sauran takwarorinsa da su dauki mataki kannmasu tsananin ra'ayi kan musulmai da larabawa a Amerika. Matukar aka dauki mataki a hukumce ta hanyar kotun koli a Amerika kan takurawar da ake yi wa musulmi da larabawa a Amerika hakan zai taimaka matuka gayya kan halin dar dar da ke wanzuwa a tsakanin al'ummar kasar Amerika.
592305