Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani rahoto da kamafanin dillancin labaran bernama ya bayar ya yi nuni da cewa, majalisar kungiyoyin da cibiyoyin musulunci a kasar Malazia za ta aike da taimako zuwa ga al'ummar yankin zirin Gaza a cikin watan Ramadana mai zuwa. Bayanin ya ci gaba da cewa babban daraktan majalisar Muhammad Azmi Abdulhamid shi ne ya sanar da hakan a jiya, inda ya bayyana cewa za a shigar da wannan taimako ne ta hanyar mashigar Rafah. 598662