Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga reshen yada labaransa na birnin Beirut da ke kasar Labanan cewa, Sayyid Ali Makki, mamba a majalisar malaman shi'a a kasar Labanan kuna daya daga cikin malaman addinin muslunci a Labanan ya bayyana cewa, tunkarar zalunci da danniyar yahudawan sahyuniya na bukatar hadin kan musulmi da kirista. Ya ci gaba da cewa a yau an wayi gari hadin kai tsakanin musulmi da kiristoci ya zama wajibi fiye da kowane lokaci, domin fuskantar barazar yahudawan sahyuniya a kan wurarensu masu tsarki.600608